in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Djibouti ya gana da wakilin kwamitin tsakiya mai kula da harkokin sojin Sin
2015-11-08 13:55:58 cri
A ran 7 ga wata da safe, shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh ya gana da wakilin kwamitin tsakiya mai kula da harkokin sojin kasa na Sin, kana babban hafsan kwamitin Fang Fenghui, wanda a halin yanzu ke ziyarar aiki a kasar Djibouti.

A yayin ganawar tasu, shugaba Guelleh ya bayyana cewa, cikin 'yan shekarun nan, kasashen biyu sun samu ci gaba bisa hadin gwiwarsu a fannonin siyasa, tattalin arziki, tsaro da sauransu, haka kuma, kasarsa na godiya ga fahimta da goyon baya da kasar Sin ta baiwa kasarsa, yana fatan iri wannan zumunci zai ci gaba da kasancewa a tsakanin kasashen biyu.

A nasa bangaren kuma, janar Fang Fenghui ya ce, kasar Sin na fatan ci gaba da yin shawarwari da shugabannin kasar Djibouti, domin karfafa fahimtar juna da hadin gwiwa a tsakanin bangarorin biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China