in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasa da kasa sun nuna yabo kan ganawar Xi Jinping da Ma Ying-Jeou
2015-11-08 13:52:14 cri
Mr. Xi Jinping da Mr. Ma Ying-jeou, watau shugabannin bangarori biyu na kasar Sin da na mashigin tekun Taiwan na kasar Sin sun gana da juna a ran 7 ga wata a kasar Singapore, inda suka tattauna kan yadda za a iya ciyar da dangantakar babban yankin kasar Sin da yankin Taiwan na Sin gaba cikin zaman lafiya. Kuma wannan shi ne karo na farko da shugabannin bangarorin biyu suka gana da juna bayan shekarar 1949.

Dangane da lamarin, majalisar gudanarwar kasa ta Amurka ta fidda wata sanarwar da ta nuna maraba da ganawar shugabannin biyu, a sa'i daya kuma, tana maraba da babban ci gaban da aka samu kan dangantakar bangarorin biyu.

Kana, ma'aikatar harkokin wajen kasar Faransa ta fidda wata sanarwa cewa, ganawar tsakanin shugabanni Xi Jinping da Ma Ying-Jeou za ta ciyar da zaman lafiya, shawarwari da hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu gaba.

Haka kuma, kakakin hukumar harkokin wajen kungiyar EU ya bayyana cewa, ganawar shugabannin bangarorin biyu ta kasance wani babban ci gaban da aka samu.

Ban da haka kuma, al'ummomin kasa da kasa na yaba wa ganawar shugabannin biyu sosai, ana kuma ganin cewa, lamarin na dauke da babbar ma'ana cikin tarihi, ana da imani cewa, za ta ciyar da dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu gaba, da kuma ba da gudummawa wajen cimma zaman lafiya da zaman karko cikin kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China