in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping da matarsa sun halarci liyafar da Sarauniya Elizabeth II ta Birtaniya ta shirya
2015-10-21 10:26:44 cri
A ranar Talata 20 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da Uwargidansa Peng Liyuan sun halarci liyafar maraba da zuwansu da sarauniyar Birtaniya Elizabeth II ta gudanar a fadar Buckingham, tare da mai gidan ta yarima Phillip, da sauran iyalai na yarima William da matarsa, gimbiya Anne Elizabeth Alice Louise Laurence, yarima Andrew, yarima Edward da suka maraba da zuwa shugaba Xi Jinping da matarsa.

Sarauniya Elizabeth II ta bayyana a cikin jawabinta cewa, shekarar bana shekara ta musamman ce ga dangantakar dake tsakanin Birtaniya da Sin, tare da hadin gwiwa da sada zumunta a tsakaninsu. Ziyarar shugaba Xi Jinping a kasar Birtaniya tana da babbar ma'ana, wadda ta sa kaimi ga raya dangantakar sada zumunta a tsakaninsu.

Shi ma a nashi jawabin Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, a matsayin kasar kawancen yaki da Fascist a yakin duniya na biyu, jama'ar kasashen Sin da Biryaniya sun nuna goyon baya da juna. A matsayin kasashen farko da kafa MDD da kasashen kwamitin sulhun MDD na dindindin, kasashen biyu suna daukar alhakin sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwa a duniya tare. Ana bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wanda zai amfanawa kasashen biyu har ma ga dukkan duniya gaba daya.

Tawagar Shugaba Xi da suka hada da Wang Huning, Li Zhanshu, Yang Jiechi tare da firaministan kasar Birtaniya David Cameron da shugaban jam'iyyar kwadago ta kasar Birtaniya Jeremy Corbyn sun halarci liyafar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China