in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Syria sun fara mai da martani kan 'yan ta'adda tare da taimakon Rasha
2015-10-17 13:46:07 cri
Shugaban sashen yaki ta babbar hedkwatar ba da nasiha ga rundunar soja ta kasar Rasha Andrey Kartapolov ya bayyana a yayin taron manema labarai da aka yi a birnin Moscow a ran 16 ga wata cewa, kasar ta cimma babbar nasara cikin hare-haren sama da ta kai ga 'yan ta'adda dake kasar Syria. Haka kuma, bisa taimakon da kasar Rasha ta yi mata, rundunar sojan gwamnatin kasar Syria ta fara mai da martani kan 'yan ta'adda, musamman ma a yankin arewacin kasar, domin dawo da matsuguna da dama daga hannun 'yan ta'adda.

Bisa labarin da aka samu daga rundunar sojan kasar Syria, an ce, Syria sun fara kai farmaki a birnin Aleppo dake arewacin kasar a ranar Jumma'a 16 ga wata, ya zuwa yanzu, sun riga sun sami iko kan wasu garuruwan dake kudancin birnin .

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha, kana wakilin musamman na shugaban kasar kan harkokin yankin Gabas ta tsakiya Mikhail Bogdanov ya bayyana cewa, ya kamata bangarorin kasa da kasa, shiyya-shiyya da kuma na kasar Syria su hada kai wajen yaki da 'yan ta'adda dake kasar Syria.

Bugu da kari, ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta fidda wata sanarwa a jiya Jumma'a cewa, Mikhail Bogdanov ya gana da jakadan kasar Syria dake kasar Rasha Riad Haddad a wannan rana, inda suka yi musayar ra'ayi kan halin da kasar Syria take ciki a halin yanzu.

Haka kuma a lokacin tattaunarwa, sun cimma matsayi daya cewa, ya kamata bangarorin kasa da kasa da kuma shiyya-shiyya da na kasar Syria su yi hadin gwiwa wajen yaki da 'yan ta'addan dake kasar Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China