in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin kasar Syria sun fara kai hare-hare ga jihar Hama
2015-10-08 11:17:46 cri
Bisa labarin da bangaren sojin kasar Syria ya bayar, an ce, sakamakon taimakon sojojin sama na kasar Rasha, sojojin kasa na gwamnatin kasar Syria sun fara kai hare-hare ga karkarar dake arewacin jihar Hama ta tsakiyar kasar Syria a ranar Laraba.

Wani jami'in bangaren soja na kasar Syria ya bayyana wa 'yan jarida cewa, wannan ne karo na farko da sojojin gwamnatin kasar suka dauki matakin soja a karkashin taimakon sojojin sama na kasar Rasha kan garuruka biyu dake karkara ta arewacin jihar Hama wadanda dakarun kawancen masu adawa suka mallaka, burinsu shi ne mallake hanyoyin dake tsakanin jihar Hama da ta Homs.

Bisa sanarwar da ma'aikatar tsaron kasar Rasha ta bayar a ranar Laraba, an ce, bangaren sojin kasar Rasha ya tura jiragen saman yaki don lalata wurare da dama dake karkashin mallakar kungiyar IS.

Sojojin saman kasar Rasha sun fara taimakawa sojojin kasar Syria wajen kai harin sama ga wuraren kungiyar IS tun daga ranar 30 ga watan Satumba. Shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya amince tare da nuna yabo ga harin sama da sojojin saman kasar Rasha suka kai a hirar shi da manema labarai na kasar Iran a kwanakin baya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China