in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Isra'ila sun kai hari kan wasu wuraren a kasar Syria
2015-08-21 10:28:23 cri
Kakakin sojojin kasar Isra'ila ya tabbatar a daren jiya Alhamis cewa sojojin kasar sun kai hari kan wasu wurare 14 a kasar Syria a matsayin mayar da martani kan harin makaman roka da aka kai mata daga kasar Syria.

Sojojin kasar Isra'ila sun bayyana a cikin wata sanarwa cewa, a ranar 20 ga wata, an kai hari da makaman roka guda 4 ga arewacin kasar Isra'ila dake dab da kan iyakar kasar da Syria, ko da ya ke harin bai haddasa mutuwa ko raunatar mutum ko daya ba.

Amma Isra'ila na zargin kungiyar masu ra'ayin Jahadin Islama, da gwamnatin kasar Syria da ta kasar Iran suke mata goyon baya, ta kai wannan hari, kana ta bukaci gwamnatin kasar Syria da ta dauki alhakin kai harin. Ya zuwa yanzu, ba a san ko akwai 'yan kasar Syria da suka mutu ko raunata a sakamakon harin sojojin Isra'ila ba.

Hakazalika kuma, sojojin kasar Isra'ila sun girke na'urorin kakkabo makaman roka a birnin Ashdod da Beer Sheva dake kudancin kasar don magance yiwuwar tsanantar halin da ake ciki a sakamakon shakkun tunanin mutuwar wani Bafalesdine da ake tsare da shi a zirin Gaza saboda kin cin abinci da ya yi na tsawon lokaci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China