in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hare-hare a Jerusalem
2015-10-11 14:23:07 cri
A ran 10 ga wata, sau biyu hare-hare suka auku a wajen kofar tsohon gari na Jerusalem, Damascus, inda Falesdinawa suka kai hari kan 'yan Isra'ila da wukake, lamarin da ya jikkata 'yan Isra'ila guda biyar, yayin da aka kashe 'yan Falesdinawan biyu da suka kai harin.

Ban da haka kuma, rikici ya barke tsakanin 'yan sandan Isra'ila da Falesdinawa a sansanin 'yan gudun hijira na Shufat dake gabashin Jerusalem, haka kuma, zirga-zirga da tashe-tashen hankulan suna ci gaba da karuwa a wasu biranen Larabawa dake Jerusalem.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya fidda wata sanarwa a ran 10 ga wata, inda ya sanar da cewa, gwamnatin kasar ta tsai da kudurin aike da karin 'yan sanda da dama zuwa Jerusalem, da kuma kara aike da 'yan sanda zuwa yankunan dake fi fama da rikice-rikice.

Bugu da kari, ya yi suka kan Falesdinu bisa zargin tayar da rikici.

Kana, yayin da shugaban Falesdinu Mahmoud Abbas ya yi shawarwari da ministan harkokin wajen kasar Amurka John Kerry ta wayar tarho a ran 10 ga wata, ya bayyana cewa, ya kamata Isra'ila ta hana Yahudawa da su ci gaba da kai wa 'yan Falesdinawa hari bisa kariyar da sojojin suka yi musu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China