in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dole ne a kokarta samun babban ci gaba a fannonin tattalin arziki da zaman al'umma a jihar Tibet cikin dogon lokaci
2015-09-08 20:28:40 cri
Shugaban majalissar bada shawara kan harkokin siyasar kasar Sin Yu Zhengsheng, ya jaddada cewa yanzu abin dake gaban komai shi ne shugabannin al'ummomin jihar Tibet su tabbatar da aiwatar da ra'ayin taron karawa juna sani kan harkokin jihar Tibet karo na 6, wanda ya bayyana kalaman shugaban kasar Sin Xi Jinping, bisa tsarin "Yayin da ake kulawa da kasa, wanda ya nuna cewa dole ne a kula da yankunan iyakar kasa tukuna, kuma yayin da ake kulawa da yankunan iyakar kasa, dole ne a kula da jihar Tibet tukuna". Shugaba Xi ya nuna cewa hakan zai taimaka wajen kokarin tabbatar da kwanciyar hankali, da samun babban ci gaba a fannonin tattalin arziki, da ma zamantakewar al'umma a jihar cikin dogon lokaci.

Mr. Yu ya bayyana hakan ne a Talatar nan a birnin Lhasa, yayin da yake sauraron rahoton aikin kwamitin JKS na jihar Tibet mai cin gashin kanta, da na gwamnatin jihar. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China