in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci al'ummar yankin Tibet da su gudanar da harkokin addini bisa doka
2015-09-08 13:33:59 cri
Babban mai ba da shawara kan harkokinn siyasa na kasar Sin Yu Zhengsheng ya yi kira ga al'ummar yankin Tibet da su rika tafiyar da harkokin addini kamar yadda dokokin addinin Buddah a yankin suka tanada.

Yu wanda ya bayyana hakan a yankin Tibet na kasar Sin, ya kuma yi kira da a rika warware matsaloli bisa doka tare da gudanar da harkokin Ibada bisa tsarin addinin Buddah.

Ya kuma bayyana matsayin kasar Sin na ci gaba da sanya kafar wando guda da masu kokarin kawo mata baraka ta kowace fuska.

Jami'in ya ce, za a dauki wannan mataki ne bisa doka ta yadda za a samar da zaman lafiya a yankin da kuma hadin kai a kasa baki daya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China