in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jaridar People Daily ta wallafa bayani game da bikin murnar cika shekaru 50 da kafa jihar Tibet mai cin gashin kanta
2015-09-08 18:08:06 cri
A gobe Talata 8 ga watan Satumbar nan ne jaridar People Daily ta nan kasar Sin, za ta gabatar da wani bayani mai taken 'Tsayawa tsayin daka kan hanyar raya jihar Tibet- da taya yankin murnar cika shekaru 50 da cin gashin kai'.

Bayanin ya bayyana yadda shekaru 50 da suka wuce kawo yanzu, kafuwar jihar Tibet mai cin gashin kanta ta bude wani sabon babi, ta yadda jama'ar yankin suka zama mutane masu dogaro da kai, suka mike daga halin matalauci zuwa yanayin wadata, da kuma sauyi daga yanayin rufe kofa zuwa bude kofa.

A cikin shekaru 50 da suka gabata, bisa jagorancin kwamitin tsakiyar JKS, da kuma goyon baya daga daukacin jama'ar sauran yankunan kasar Sin, da kokarin jama'ar jihar Tibet, an cimma burin hada kan al'ummomi, da samun jituwar zaman al'umma, tare da samun babban ci gaba wanda ba a taba ganin irinsa ba kafin aiwatar da kwaskwarimar demokuradiyya.

Bayanin ya nuna cewa hakan muhimmin sauyi ne a tsarin gurguzu mai matukar fifiko. Kaza lika tsarin kulawa da jihohi, da al'ummomi da kansu, tsari ne da ya dace, wanda kuma aka yi amfani da shi wajen daidaita batun al'ummomi a kasar Sin. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China