in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta shirya bikin cika shekaru 70 da kawo karshen yakin duniya na biyu a birnin Beijing
2015-09-01 20:23:40 cri
Ranar 3 ga watan Satumba rana ce ta cikon shekaru 70 da kawo karshen yakin duniya na biyu kana ranar da Sinawa suka samu nasara a kan mayakan kasar Japan. Da karfe 10 na safiyar wannan rana, za a gudanar da wani kasaitaccen bikin a dandalin Tian'anmen dake birnin Beijing don tunawa da wannan rana mai muhimmanci.

A lokacin ne kuma, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gabatar da wani jawabi mai muhimmanci, kana ya kalli faretin rundunonin sojan kasar.

Haka kuma, a wannan rana, Gidan Rediyon CNR, Gidan Talabijin na kasar Sin CCTV da kuma Gidan Rediyon CRI za su watsa abubuwan da ke faruwa a kan bikin kai tsaye ga duniya. Hakazakila shafin intanet na Renmin, Xinhua da kuma Gidan talebijin ta intanet na kasar Sin da kuma shafin intanet na kasar Sin su ma za su watsa dukkan abubuwan da ke wakana a dandalin kai tsaye. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China