in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin ta yi bayani kan batun bude shafin tsibirin Diaoyu a tashar yanar gizo ta majalisar ministocin Japan
2015-08-29 12:54:31 cri
A daren jiya Jumma'a 28 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, madam Hua Chunying ta amsa tambayar 'yan jarida dangane da ko gwamnatin Japan ta bude wani shafi na musamman kan tarihin tsibirin Diaoyu na kasar Sin, da na tsibirin Dokdo na kasar Koriya ta Kudu a tashar yanar gizo ta majalisar ministocin gwamnatin kasar Japan.

Madam Hua ta furta cewa, tun asali kasar Sin ke da mallakar tsibirin Diaoyu, don haka take kalubalantar Japan da ta daina duk ayyukan mamaye ikon mallakar cikakken yankin kasa na Sin.

Ban da haka, madam Hua ta jaddada cewa, kowace hanyar da Japan za ta bi domin yada jita-jita, ba za a canza ainihin tarihi na cewa, tun asali Sin ce ta mallaki tsibirin Diaoyu.

Ta ce, Sin na kalubalantar Japan da ta amince da ainihin tarihi, ta daina yunkurin mallakar cikakken yankin kasar Sin. (Fatima Liu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China