in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta amsa tambayoyi game da ziyarar da matar firaministan Japan ta kai a haikalin Yasukuni
2015-08-21 13:15:43 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bukaci kasar Japan da ta waiwayi tarihi game da hare-haren da ta kai, sannan ta yi watsi da ra'ayin nuna karfin soja.

Madam Hua ta bayyana hakan ne a gun taron manema labaru a yayin da aka yi mata tambaya game da ra'ayin Sin kan batun ziyarar da mai dakin firaministan kasar Japan Akie Abe ta kai wurin ibadar Yasukuni nan da ake takaddama a kai a ranar 18 ga wata.

Hua ta kara da cewa, kamata ya yi kasar Japan ta waiwayi tarihinta na kai hare-haren da ta aikata, da gudanar da ayyukan kara imani da samun sulhuntawa a tsakaninta da kasashen Asiya dake makwabtaka da ita. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China