in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin jakadanci na Sin a Nijeriya ya kira taron kamfanonin Sin a Nijeriya a tsakiyar shekarar 2015
2015-08-23 13:34:27 cri
A ranar Jumma'a 21 ga wata, a birnin Abuja, ofishin jakadanci na Sin a Nijeriya ya kira taron kamfanonin Sin a Nijeriya a tsakiyar shekarar 2015, inda wakilai daga kamfanonin Sin a kasar sama da 70 suka halarci taron.

A gun taron, jakadan Sin a Nijeriya, Gu Xiaojie ya yi jawabi, inda ya waiwayi yanayin da ake ciki a Nijeriya a farkon rabin shekarar bana a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da kuma tsaro, tare da yin nazari kan sabbin matakan da aka dauka a fannonin tsaron kasa, da yaki da cin hanci da rashawa da kuma raya tattalin arziki a karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari. Jakada Gu ya ce, sabuwar gwamnatin kasar Nijeriya za ta kafa majalisar ministoci nan ba da dadewa ba, daga bisani za ta gabatar da sabbin manufofi da cika alkawarinta na yin gyare-gyare a kasar. A sabili da haka, jakada Gu ya sa kaimi ga kamfanonin Sin a Nijeriya da su yi imani cewa, akwai makoma mai kyau wajen yin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da gudanar da ayyukansu bisa doka.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China