A yayin bikin kaddamar da aikin gina tashar da aka yi a wannan rana, shugaba Museveni ya bayyana godiya sosai ga gwamnatin kasar Sin kan babban taimakon da ta samar wajen raya aikin samar da wutar lantarki mai amfani da karfin ruwa a kasar Uganda. Yana imani cewa, tashar ta Isimba za ta sassauta matsalar karancin wutar lantarki da ake fama da ita a kasar, lamarin da zai taimakawa kasar wajen raya masana'antu da kuma kyautata zaman rayuwar al'ummomin kasar.
Rahotanni na cewa, kamfanin samar da wutar lantarki bisa karfin ruwa na kasar Sin wato CWE ne ya dauki nauyin gina tashar ta Isimba da ke kasar Uganda, aikin da ake saran zai lashe dallar Amurka miliyan 568 kuma ana fatan kammalarsa a shekarar 2018. (Maryam)