in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Syria ya sake ba da umurnin yin afuwa
2015-07-26 13:45:35 cri
A jiya Asabar 25 ga wata, shugaban kasar Syria Bashar Assad ya ba da umurnin yin afuwa ga mutane wadanda aka cafke sakamakon keta dokar shiga rundunar soja da dokar hukunta laifuffukan soja da sauransu.

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Syria ya bayar, an ce, bisa wannan umurni, za a yi wa mutanen da suka yi gudun shiga rundunar soja da sauransu afuwa daga wannan rana. Kuma an ba da kwanaki 30 zuwa 60 ga wadanda suke gudu a cikin gida da kuma ketare, idan sun je ofishin 'yan sanda da kansu cikin lokaci, za a yi musu afuwa.

Masu fashin baki sun bayyana cewa, makasudin ba da wannan umurnin shi ne kara samun yawan sojoji a Syria. Bisa alkaluman da kungiyar sa ido kan hakkin bil'adam a Syria da aka kafa hedkwatarta a birnin London ta bayar, an ce, tun bayan barkewar rikici a Syria a watan Maris na shekarar 2011 zuwa yanzu, matasa kimanin dubu 70 sun yi gudun shiga aikin soja a kasar.

Kuma bayan barkewar rikicin Syria, shugaban kasar Bashar Assad ya sha daukar irin wannan mataki sau da dama.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China