in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kira sabon zaman shawarwari game da batun Syria a birnin Geneva
2015-05-02 16:52:41 cri
Ofishin kula da harkokin MDD dake birnin Geneva na kasar Switzerland, ya ce za a bude sabon zaman gudanar da shawarwari game da batun kasar Syria a birnin Geneva, taron da za a kwashe kwanaki biyar ko shida ana gudanarwa tun daga ranar 4 ga watan nan na Mayu.

Kaza lika ofishin ya rawaito manzon musamman na babban magatakardan MDD kan batun Syria Steffan de Mistura, na cewa za a gayyaci bangaren gwamnatin kasar Syria, da wakilan kungiyoyin 'yan adawa, da kuma wakilan jama'ar kasar ta Syria, da ma wasu wakilan shiyya-shiyya da na kasa da kasa wadanda abin ya shafa, inda za su tattauna yanayin da kasar ke ciki a halin yanzu.

Har wa yau ana fatan gabatar da shawarwari game da yadda za a iya aiwatar da kudurorin dake kunshe cikin yarjejeniyar Geneva kan batun kasar ta Syria da aka kulla a baya.

Bugu da kari, rahoton ofishin ya ce, za a gudanar da shawarwarin na wannan zagaya a asirce, kana ba za a fidda sanarwar kafin, ko bayan kammalar taron ba. Sai dai bayan kammalarsa, Mr. Mistura zai gabatar da sakamakon shawarwarin da aka cimma ga babban magatakardan MDD. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China