in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS na shirin musayar wasu firsunoni data kama idan aka ba ta 'yar kunar bakin wake
2015-01-29 16:23:06 cri
Wata mata ma'abuciyar harin kunar bakin wake a yanzu haka ta isa yankunan Syria, a wani kokari da kungiyar IS take yi na ganin cewar gwamnatin Jordan ta mika mata matar a madadin wasu mutane guda biyu da ta kama wadanda kuma take yin garkuwa da su.

Wani rahoton gidan talabijin na al-Mayadeen ya ce kungiyar IS zata yi musayar dan kasar Japan da wani matukin jirgin saman kasar Jordan da ta kama idan Jordan ta mika mata matar mai suna Sajida al-Rishawi.

Rahotannin sun ce kungiyar IS na sa ran ganin Jordan ta saki matar wacce aka tsare a gidan kaso na Jordan bayan da ta taka rawa a wani harin kunar bakin wake a Amman a watan Nawumbar shekarar 2005, to amma daga baya sai ta tsira da ranta bayan bam din da ta yi damara da shi ya ki tashi.

Daga baya gwamnatin Jordan ta kama matar kuma wata kotun soji ta yanke mata hukuncin kisa a watan satumbar shekarar 2006, to amma matar ta daukaka kara har sau biyu.(Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China