in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron AU game da yadda za a taimakawa kasashen da cutar Ebola ta yi barna
2015-07-20 20:15:01 cri
A yau ne aka kaddamar da taron kasa da kasa da kungiyar tarayyar Afirka AU ta shirya don musayar ra'ayoyi a yakin da Afirka ke yi da cutar Ebola.

Bugu da kari taron da aka bude yau a birnin Malabo, fadar mulkin Equatorial Guinea zai kuma tattauna yadda kasashen da cutar ta fi yi wa illa ke farfadowa.

Taron na yini biyu mai taken "taimakawa kasashen Afirka wajen farfadowa tare da sake gina kasa bayan cutar ta Ebola" zai kuma hallara kan jami'an gwamnatoci, hukumomin MDD da na shiyya-shiyya, da kuma sassa masu zaman kansu, inda ake sa ran za su kara yin musayar ra'ayoyi game da irin darussan da aka koya a yaki da cutar Ebola.

Ana kuma sa ran taimakawa kasashen da cutar ta fi yi wa ta'adi, musamman kasashen Guinea, Liberia da Saliyo ta yadda za su farfado da kuma kara matakan kantagarkin barkewar cutar a nahiyar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China