in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a fara gwajin allurar rigakafin cutar Ebola a kasashe da dama
2015-07-18 13:38:54 cri
Jiya Jumma'a 17 ga wata, jami'ar Oxford ta Birtaniya ta ba da sanarwar cewa, an shiga mataki na biyu a nazari kan allurar rigakafin cutar Ebola da manazarta na Birtaniya da Faransa suke yi, wato za a fara gwajin allurar a kan mutane a kasashe da dama.

Jami'ar Oxford ta bayyana cewa, manazarta suna shirin neman masu aikin sa kai sama da 600 a Birtaniya da Faransa, wadanda ke da lafiya, domin shiga wannan aikin gwajin allurar. Bayan haka, za a gudanar da gwajin allurar a kasashen yammacin Afirka da cutar Ebola ke fi yaduwa.

A cikin mataki na farko da aka yi, an yi gwajin allurar ga masu aikin sa kai na Birtaniya 87. Sakamakon da aka samu ya nuna cewa, allurar na da amfani, kuma babu wata illar mai tsanani da ta kawo wa jikin mutanen da aka gwajin kansu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China