in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta samar da karin taimakon kudin dallar Amurka miliyan 5 domin fuskantar da Ebola
2015-07-11 13:34:36 cri
Jiya Jumma'a 10 ga wata, an kira taron farfadowar yankunan da suka taba fama da cutar Ebola na duniya a hedkwatar MDD dake birnin New York, inda zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana cewa, domin nuna goyon baya ga MDD da ta ci gaba da ayyukan ba da jagoranci da shiga tsakani cikin yunkurin farfadowar yankunan da suka taba fama da yaduwar cutar Ebola, gwamnatin kasar Sin za ta samar da karin taimakon kudi na dallar Amurka miliyan 5 ga Asusun ajiya na amintattu na fuskantar da cutar Ebola na MDD.

Liu Jieyi ya bayyana cewa, a matakin gaba, kasar Sin za ta samar da taimako ga yankunan da suka taba fama da cutar Ebola bisa bukatunsu, domin samar da goyon baya da kuma halartar ayyukan kafuwar tsarin yin rigakafi kan cututtuka da kuma samar da kayayyakin ba da agaji da kiwon lafiya a nahiyar Afirka, ta yadda za a iya kyautata kwarewar kasashen Afirka wajen fuskantar hadarin kiwon lafiya na gaggawa.

Bugu da kari, Liu Jieyi ya ce, babban tushen farfado da yankunan shi ne ciyar da tattalin arzikin zaman takewar al'umma gaba, ya kamata gamayyar kasa da kasa su ba da taimako ga kasashen yankunan da suka taba fama da cutar Ebola wajen fuskantar hadarurruka daga dukkan fannonin domin tabbatar da dauwamammen ci gaba wadannan kasashe. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China