in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Lebanon ta sake jinkirta babban zaben shugaban kasar
2015-07-16 14:01:30 cri
A jiya ne majalisar dokokin kasar Lebanon ta sanar da sake jinkirta ranar zaben shugaban kasar, sabo da adadin 'yan majalisar dokoki da suka kada kuri'u bai kai adadin da aka tsara bisa dokar kasa ba. Wannan shi ne karo na 26 da majalisar ke jinkirta zaben tun watan Afrilu na shekarar da ta gabata.

Kuma bisa kundin tsarin mulkin kasar Lebanon, majalisar dokokin kasar ce ke zabar shugaban kasar, amma sai an samu kashi biyu bisa uku na 'yan majalisar kafin majalisar dokokin kasar ta kada kuri'ar zaben shugaban kasar.

Adadin 'yan majalisar dokokin kasar na wannan karo guda 128 ne, amma adadin 'yan majalisar da suka kada kuri'u a ran 15 ga wata 46 ne kawai, don haka bai kai adadin da kundin tsarin mulkin kasar ya tsara ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China