in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Hezbollah za ta shiga sabuwar gwamnatin kasar Lebanon
2014-02-17 10:56:43 cri
Hassan Nasrallah, babban sakataren kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon, ya furta a ranar Lahadi 16 ga wata a birnin Beirut, fadar mulkin kasar, cewa kungiyar za ta nuna yakini a kokarin shiga sabuwar gwamnatin kasar.

Nasrallah ya bayyana hakan ne a shirin wani gidan telabijin na kungiyar Hezbollah, inda ya ce kungiyar ba ta da ra'ayin nuna hamayya yayin da take neman shiga cikin sabuwar gwamnatin. Maimakon haka, tana son samun damar hadin kai, da samun masalaha, da yin mu'amala a tsakanin bangarorin kasar daban daban, a kokarin magance cacar baki, wanda a cewarsa ya dace da moriyar dukkan bangarorin. Sa'an nan, mista Nasrallah ya nuna fatansa na ganin sabuwar gwamnatin za ta yi kokarin dakile duk wani nau'in aikin ta'addanci, da warware matsalolin da kasar ke fuskanta a fannonin tattalin arziki da zaman takewar al'umma.

Kafin haka, shugaban kasar Lebanon Michel Suleiman ya sanar da kafuwar sabuwar gwamnatin kasar karkashin jagorancin firaminista Tammam Salam a ranar 15 ga wata, lamarin da ya kawo karshen halin kiki-kaka a fannin siyasar kasar wanda aka yi watanni 10 ana fama da shi. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China