in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yi Allah wadai da harin da kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta kai wa sojojin kasar Lebanon
2014-08-05 11:03:31 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya bayar da wata sanarwa a ranar 4 ga wata, inda ya yi Allah wadai da harin da kungiyar masu tsattauran ra'ayi ta kai wa sojojin kasar Lebanon a yankin Aarsal dake kasar.

Sanarwar ta ce, harin da aka kai a ranar 2 ga wata ya haddasa mutuwar sojoji a kalla 14, tare da jikkata wasu 86 kana 22 suka bace, baya ga fararen hula da suka mutu ko suka ji rauni.

Kwamitin sulhu ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a sakamakon harin da aka kai wa sojojin gwamnatin kasar ta Lebanon.

Ban da wannan kuma, kwamitin sulhu ya jaddada cewa, zai goyi bayan gwamnatin kasar Lebanon a wannan lokaci, kana ya yi kira ga majalisar dokokin kasar da ta tabbatar da gudanar da zaben shugaban kasar kamar yadda aka tsara. Sannan kwamitin sulhun ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su hada kai yayin da 'yan aware ke kokarin raba kan kasar, da kuma bin manufar hana tsoma baki kan rikicin kasar Syria. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China