Bisa labarin da aka samu, an ce, dakarun magoyon bayan kungiyar Ansar Bayt al-Maqdis ne da suka bada yardarsu ga kungiayr IS.
Haka kuma, a wannan rana, shugaban kasar Masar Abdelfattah al Sisi ya kai ziyara ba zata a arewacin lardin Sinai, inda ya kai ziyara ga rundunonin sojoji da 'yan sanda da aka jibge wurin, ya kuma sa kaimi ga jami'an tsaron dake yaki da ta'addanci cewa, suna gudanar da aiki mai girma wajen kiyaye tsaron kasar.
A ran 1 ga watan Yuli, an kai harin ta'addanci mai tsanani a arewacin lardin Sinai a kasar Masar, inda 'yan bindiga suka kai hare-hare kan tashoshin gudanar da binciken soja a dama a wurin, inda kuma daga bisani kungiyar Ansar Bayt al-Maqdis ta sanar da daukar alhakin wadannan hare-hare . (Maryam)