in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bai dace Amurka ta koyar da darasin hakkin dan Adam ba
2015-06-26 18:29:06 cri
Rahoton yanayin hakkin dan Adam na kasa da kasa da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta fidda kwanan baya, ya sake yin suka kan yanayin hakkin dan Adam na kasar Sin.

Dangane da lamarin, yau Jumma'a 26 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yayin taron mamema labaran da aka yi a birnin Beijing cewa, al'umma'ar kasar ta Sin su ne suke da ikon fadi yanayin hakkin dan Adam da ake ciki a kasarsu, amma bai kamata kasar Amurka ta koyar da darasin hakkin dan Adam a nan duniya ba. Mr. Lu ya ce kasar Sin na fatan Amurka ta iya kula da harkokin cikin gidanta yadda ya kamata, ta kuma daina tsoma baki cikin harkokin ketare.

Haka kuma Kasar Sin tana son yin shawarwari tare da kasashen ketare bisa akidar adalci da kuma na girmama juna kan batun hakkin dan Adam. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China