in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi a girmama hanyoyin da kasashe ke bi yayin da ake kokarin inganta sha'anin kare hakkin dan Adam
2014-10-30 15:43:32 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin a MDD Wang Min ya bayyana cewa, kasashen duniya na da ikon zaben hanyoyin inganta sha'anin kare hakkin dan Adam, da suka dace da su da ma muhimman ayyukan dake da alaka da hakan. Don haka ya kamata a girmama irin wadannan hanyoyi da kasashe mabanbanta ke bi yadda ya kamata.

Mr. Wang ya bayyana hakan ne yayin zaman babban kwamitin majalisar MDD wanda ya maida hankali, ga gudanar da muhawara kan batun kare hakkin dan Adam, inda ya ce kasar Sin tana fatan ganin ta kara kaimi ga samun bunkasuwa tare da ragowar sassan duniya baki daya. Kuma samun ikon rayuwa da ikon samun bunkasuwa shi ne kan gaba ga kasashe masu tasowa da za su gudanar a fannin kare hakkin dan Adam.

Ban da wannan kuma, Wang Min ya ce, sha'anin kare hakkin dan Adam muhimmin kashi ne na inganta tattalin arziki, da zamantakewar al'ummar kasar Sin. Ya ce a kokarinta, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa mai alamar kasar Sin kan kare hakkin dan Adam, matakin da ya tabbatar da ikon bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al'umma da al'adunsu, dama na hakkin jama'ar da kuma na ikon siyasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China