Sudan ta nuna bacin ranta game da yadda Amurka ta sanya ta cikin jerin kasashen da ke goyon bayan 'yan ta'adda
Rahotanni daga Sudan na cewa, gwamnatin kasar ta nuna bacin ranta game da yadda kasar Amurka ta shigar da kasar cikin jerin kasashen dake goyon bayan ta'addanci, tana mai cewa kasar Amurka ba ta mata adalci ba.
Wani rahoto da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta fidda kwanan baya, kasar Amurka ta sake sanya sunan kasar Sudan cikin jerin kasashen dake goyon bayan ayyukan ta'addanci, tana mai cewa, gwamnatin kasar Sudan tana da alaka da wasu kungiyoyin 'yan ta'addan kasar. (Maryam)