in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fiye da 'yan Sudan ta Kudu dubu 14 suka gudu zuwa Sudan
2015-06-14 13:23:24 cri
Kungiyar 'yan gudun hijira ta MDD (HCR) ta sanar a ranar Asabar cewa fiye da fararen hula na Sudan ta Kudu dubu 14 suka tsere zuwa Sudan a tsawon makwanni biyu na baya bayan nan dalilin rikicabewar tashe tashen hankali a yankunan dake da arzikin man fetur na kasarsu.

A wannan mako na baya, mun lura da kwararar mutane kimanin dubu 7 da kuma wadannan makwanni biyu na baya kimanin mutane dubu 14 suka iso, lamarin da muke ganin wata matsala cikin wata matsalar, in ji madam Ann Encontre, jami'ar da ke kula da harkokin 'yan gudun hijira ta HCR game da Sudan ta Kudu.

Madam Ann ta kara da cewa yawancin 'yan kasar Sudan ta Kudu da suka bar kasarsu mata ne da yara kanana da suka gujewa tashe tashen hankali a cikin jihohin Haut-Nil da Unite, yankunan da ke da arzikin man fetur.

Sudan ta karbi 'yan Sudan ta Kudu fiye da dubu 157 da suka bar kasarsu da ke fama da riciki, kuma kungiyoyin MDD dake aiki a Sudan sun nuna damuwa a baya bayan nan kan rashin kudin gudanar da aiki domin biyan bukatun 'yan gudun hijira na Sudan ta Kudu.

Kasar Sudan ta Kudu dai ta samu 'yancin kanta a shekarar 2011, amma ta fada cikin rikici a cikin watan Disamban shekarar 2013 a yayin da yaki ya barke tsakanin dakarun dake goyon bayan shugaban kasar Salva Kiir da sojoji masu biyayya ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Riek Machar.

Rikicin yayi saurin rikidewa a wani yakin da ya shafi kasar baki daya, tashen tashen hankali suka koma rikicin kabilanci inda 'yan kabilar Dinka ta shugaban kasa ke yaki da kabilar Nuer ta Riek Machar.

Wadannan tashe tashen hankali sun hadasa mutuwar miliyoyin jama'ar Sudan ta Kudu, da tilastawa kimanin mutane miliyan 1,9 barin gidajensu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China