Kakakin gwamnatin Sudan Ahmed Bilal Osman, ya ce ana sa ran isar shugaba Al-Bashir gida da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Litinin din nan bisa agogon birnin Khartoum.
Zuwan shugaba Al-Bashir Afirka ta Kudu dai ya yamutsa hazo, tun bayan da kotun hukunta manyan laifukan yaki ta ICC ta daga bukatar mika mata shi, bisa zargin da take masa na aikata laifukan yaki a yankin Dafur dake kasar ta Sudan.