in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kada kuri'u a babban zaben kasar Togo
2015-04-26 16:39:59 cri
A jiya Asabar ne aka gudanar da babban zaben shugabancin kasar Togo, inda kimanin jama'ar kasar miliyan 3.5 suka kada kuri'un su, a tashoshin zabe 8,994 dake sassan kasar daban daban.

Rahotanni sun nuna cewa zaben na wannan karo na kunshe ne da 'yan takara 5, ciki hadda shugaba mai ci Faure Essozimna Gnassingbe wanda ke neman zarcewa a karo na 3.

An dai fara kada kuri'un ne da karfe 7 na safiyar ranar ta Asabar, aka kuma kammala da karfe 4 na yamma. Haka kuma masu sa ido sun gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Bayan kada kuri'un an kuma fara kididdiga kamar dai yadda aka tsara tun da farko.

Kimanin masu aikin sa ido 2,506 ne suka halarci kasar ta Togo, ciki hadda jami'ai 490 daga kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, da sauran wakilai daga kungiyar ECOWAS, da na kungiyar tarayyar tattalin arziki da kudade ta yammacin Afirka UEMOA a takaice, da ma wasu kungiyoyin kasa da kasa da na shiyya-shiyya.

Kaza lika, bisa dokar zabe ta kasar Togo, ana gudanar da zagaye daya ne kadai, sa'an nan a bayyana wanda ya lashe zaben a matsayin sabon shugaban kasa, cikin kwanaki 6 da kammala kada kuri'un. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China