in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara kada kuri'u a babban zaben kasar Togo
2015-04-25 20:24:53 cri
Kimanin al'ummar kasar Togo miliyan Uku da rabi ne ake fatan za su kada kuri'unsu, a babban zaben kasar da aka fara gudanarwa a Asabar din nan.

Rahotannin sun bayyana cewa an bude rumfunan zabe 8,994 a sassan kasar daban daban, inda ake sa ran 'yan kasar za su zabi ko dai shugaba mai ci Faure Gnassingbe, ko kuma daya daga sauran 'yan takara 4 da a wannan karo ke fatan a zabe su a mukamin shugabancin kasar.

Domin cimma nasarar zaben, wakilai 2,506 daga hukumomin kasa da kasa daban daban sun hallara a kasar ta Togo, inda za su sanya ido ga gudanar zaben. Cikin wannan adadi akwai wakilai kimanin 490 da suka fito daga kungiyar AU, da kungiyar ECOWAS da ta UEMOA da dai sauran su.

Shugaba Gnassingbe dai na neman sake kasancewar shugaban kasar ta Togo ne a karo na 3, bayan da ya lashe zaben kasar a shekarar 2005, da kuma zaben 2010. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China