in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
2015: Hukumomi 23 sun yi hadin gwiwa wajen gudanar da ayyukan fadakarwa game da ikon mallakar ilmi a fadin kasar Sin
2015-04-20 16:23:29 cri
Hukumomi 23 da suka hada da hukumar kula da ikon mallakar ilmi ta kasar Sin, da ma'aikatar harkokin fadakarwa ta kwamitin tsakiya na JKS, sun gudanar da hadin gwiwa wajen gudanar da ayyukan fadakarwa game da ikon mallakar ilmi na wannan shekara, wanda za a aiwatar cikin mako guda tsakanin tun daga Litinin din nan.

A cikin makon guda, hukumomin za su yi amfani da zarafin su wajen gudanar da ayyuka kamar amsa tambayoyi, da gudanar da dandalin tattaunawa, da yin bayani a fili, da gabatar da rahoto, tare da bikin nune-nune da dai sauransu, don fadakar da ikon mallakar ilimi ga jama'ar kasar.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, an samu bunkasuwa cikin sauri game da sha'anin ikon mallakar ilimi na kasar Sin a shekarun baya baya nan. Inda a shekarar 2014, yawan neman izinin mallakar fasaha a kasar Sin ya kai dubu 928, adadin da ya karu da kashi 12.5 cikin dari bisa na makamacin lokaci a shekarar 2013, kana ya ci gaba da kasancewa a matsayin farko a duniya a wannan fanni a shekaru hudu a jere.

Kaza lika yawan tambarin ciniki da aka yi rajista a wannan shekara ya kai miliyan 8 da dubu 390, adadin da ya kai matsayin farko a duniya a wannan fanni.

Shugaban hukumar kula da ikon mallakar ilimi ta kasar Sin Shen Changyu, ya bayyana cewa ikon mallakar ilimi muhimmin tushe ne, a fannin albarkatun neman samun bunkasuwa da yin takara, kana yana taka muhimmiyar rawa wajen daukar matakan kirkire-kirkire, da sa kaimi ga bunkasar tattalin arziki mai inganci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China