in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dalibai fiye da dubu 90 sun shiga makarantar sakandare kyauta a jihar Xinjiang
2014-10-27 15:23:54 cri
A sakamakon fara aiwatar da manufar shiga makarantar sakandare kyauta da gwamnatin kasar Sin ta bullo da ita, yawan daliban da suka shiga makarantar sakandare daga makarantar midil a yankin kudancin jihar Xinjiang ya karu zuwa kashi 80 cikin dari, kuma dalibai fiye da dubu 90 daga kabilu daban daban sun iya shiga makarantar sakandare ba tare da biyan kudi ba.

Ana kiran yankin dake kudu da tsaunukan Tianshan a jihar Xinjiang da sunan yankin Xinjiang ta kudu, wanda ya hada da Kashgar, Hotan, Kizilsu Kirghiz da kuma Aksu. Kana shi ne yanki da 'yan kabilun Uygur, Kirgiz, Mongolia, da Tajik da sauran kananan kabilu ke zaune. A sakamakon rashin bunkasuwar tattalin arziki da sadarwa, shi ya sa yankin ke fuskantar koma bayan ilmi.

An ce, tun daga shekarar bana, gwamnatin tsakiya ta kasar ta baiwa ko wane dalibi dake makarantar sakandare kudin karatu na Yuan 600 a kowane zangon karatu, kana dalibai daga kauyuka ko wadanda ke fuskantar mawuyacin halin rayuwa a birane wadanda ba su iya sayen littattafan karatu na shekaru 3 wato Yuan 1300, kuma hukumar kudi ta yankin ko karamar hukumar kudi za su baiwa kowanen dalibi kudin dakin kwana a makaranta da Yuan 600 a kowace shekara. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China