in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi maraba da kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin gwamnatin Mali da 'yan adawa
2015-03-07 17:09:08 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya yi maraba da kulla yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya tsakanin gwamnatin kasar Mali da tsagin 'yan adawa mai sansani a arewacin kasar.

Cikin sanarwar da kakakinsa ya fitar, Ban Ki-moon ya ce kulla yarjejeniyar babban mataki ne na samun ci gaba a aikin shimfida zaman lafiya a duk fadin kasar ta Mali.

Ya ce burin siyasa na bangarori daban daban da batun ya shafa na da muhimmiyar ma'ana wajen cimma manufar zaman lafiya na dindindin a kasar. Don haka ya kamata bangarorin su ci gaba da dukufa, domin lalubo hanyoyin da suka dace na warware matsalar kasar daga tushe.

Daga nan sai ya bayyana burin MDD na ci gaba da goyon bayan al'ummar kasar ta Mali, wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma yadda ya kamata, ta yadda za a iya kai ga wanzar da zaman lafiya, da tsaro, da adalci da kuma ci gaba a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China