in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a samar da taimakon jin kai ga Yemen
2015-04-18 17:09:30 cri
Jiya Jumma'a 17 ga wata, hukumar taimakon jin kai ta MDD ta yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su samar da taimakon jin kai na gaggawa na dallar Amurka miliyan 274 ga kasar Yemen, domin taimaka wa jama'ar kasar da rikicin kasar ya shafa.

Kana ofishin kakakin babban magatakardan MDD ya bayyana cewa, a wannan rana, hukumar jin kai ta MDD da abokanta na samar da taimakon jin kai sun fara tattara kudade cikin gaggawa a kasar Jordan.

Kuma za a yi amfani da kudaden wajen samar wa jama'ar kasar Yemen kayayyakin agaji, ruwan sha, abinci da kuma wuraren kwana da dai sauransu.

Kaza lika, bisa kididdigar da MDD ta yi, an ce, a halin yanzu, adadin mutanen kasar Yemen dake fama da karancin abinci ya kai miliyan 12, yayin da yara kimanin dubu 160 ke fama da karancin abinci, haka kuma, ba a da isassun makamashi da wutar lantakarki a wasu yankukan kasar, kana an dakatar da samar da ruwan sha a wasu yankunan kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China