in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta gaggauta tura makamai zuwa Saudiya
2015-04-08 11:24:52 cri
A ran 7 ga wata, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Amurka Anthony Blinken ya bayyana a babban birnin kasar Saudiya, Riyadh cewa, a halin yanzu, kasar Amurka na gaggauta tura makamai zuwa kasar Saudiya, domin nuna mata goyon baya kan matakin soja take dauka kan mayakan kungiyar al-Huthiyyun ta kasar Yemen.

Bayan ganawa da wasu jami'an kasar Saudiya, mista Blinken ya bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, kasar Saudiya ta dauki matakan soja kan dakarun kungiyar al-Huthiyyun tare da goyon bayan wasu kasashe, domin nuna musu cewa, ba za a iya hambarar da wata gwamnatin kasa mai ci ba ta hanyar karfin tuwo.

Ya kuma kara da cewa, kasar Amurka na gaggauta tura makamai zuwa kasar Saudiya domin nuna mata goyon baya, haka kuma, za su yi musayar bayanai da kuma kafa wani shiri cikin hadin gwiwa game da wannan lamari.

Bugu da kari, ya ce, kasar Amurka na ganin cewa, a halin yanzu, ya zama wajibi ta karfafa hadin gwiwarta da kasar Saudiya, har ma duk kasashen mashigin teku, domin sa kaimi ga kasar Yemen, musamman ma ga kungiyar al-Huthiyyun da magoyon bayanta da su bi yarjejeniyar siyasa da aka kulla a baya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China