in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Masar yayi alkawarin kare kasashen yakin Golf gaban tabarbarewar rikicin Yemen
2015-04-05 16:51:42 cri
Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sissi ya dauki niyya a ranar Asabar wajen kare kasashen yankin Golf idan har ya zama dole, in ji kamfanin dillancin labaran kasar MENA. Kasar Masar ba zata yi watsi da 'yan uwanta ba na yankin Golfe kuma za mu kare su idan ya zama dole, in ji shugaban Masar bayan wani taron koli na manyan jami'an sojojin kasar.

Shugaba al-Sissi ya yi wadannan kalamai a lokacin da gamayyar kasashe goma da ke karkashin jagorantar Saudiyya ke kai hare hare ta sama kan mayakan shi'a na Houthis a kasar Yemen, wadanda suka karbe biranen kasar da dama tun cikin watan Satumban shekarar 2014 tare da tilastawa shugaban kasar Abd-Rabbu Manour Hadi ficewa daga kasar zuwa Riyad, hedkwatar kasar Saudiyya.

Rikicin Yemen na janyo fargaba sosai game da yiyuwar yankin mashigin ruwan Bab al-Mandab ya koma hannun mayakan Houthis da ake zaton samun goyon bayan kasar Iran da kuma ke janyo matsalar tsaro a kasashen da yankin Golfe. Kasar Iran dai ta yi watsi da zargin da ake mata na cewa tana baiwa mayakan shi'a makamai.

Kasashen Masar da Saudiyya sun tura jiragen ruwan yakinsu a mashigin ruwan Bab al-Mandab, wanda ita ce hanya guda wajen shiga yankin ruwan Suez tun daga ruwan tekun Arabic da ya kasance muhimmin wurin musanyar kasuwanci tsakanin Turai da Asiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China