in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allah wadai da harin da kungiyar Al-Shabaab ta Somaliya ta kai jami'ar Moi
2015-04-04 16:53:39 cri
Jiya Jumma'a 3 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa, inda ya yi allah wadai da babbar murya kan kungiyar tsattsauran ra'ayin addini ta Al-shabaab ta kasar Somaliya, game da harin da ta kai a jami'ar Moi dake birnin Garissa na kasa Kenya, inda ya kuma jaddada cewa, zai tsaya wa tsayin daka wajen yaki da duk wani irin ta'addanci.

Kwamitin sulhu na MDD ya nuna juyayi ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon harin, da kuma jama'a da gwamnatin kasar Kenya, haka kuma, kwamitin sulhu na MDD ya yaba wa gwamnatin kasar Kenya kan kokarin da take bayar wajen yaki da ta'adanci da kuma gudummawa da ta bayar kan aikin yaki da kungiyar Al-Shabaab na tawagar musamman da kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU ta tura zuwa kasar Somaliya.

Bugu da kari, kwamitin sulhu na MDD ya sake jaddada cewa, zai mai da martani kan kudurin aikace-aikacen ta'addanci, bisa kundin tsarin MDD.

A ranar 2 ga wata, wasu dakaru sun kai hari a jami'ar Moi dake birnin Garissa dake arewa maso gabashin kasar Kenya, inda suka halaka mutane 148, yayin da 179 suka ji rauni, sa'an nan, kungiyar Al-Shabaab ta kasar Somaliya ta sanar da daukar alhakin harin din, kana harin ya kasance harin ta'adanci mafi tsanani da kasar Kenya ta taba fama da shi, tun shekarar 2011 da kasar ta tura sojoji zuwa kasar Somaliya domin yaki da dakarun kungiyar Al-Shabaab. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China