in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sauke Al-Hasi daga mukamin firaministan gwamnatin 'yantar da jama'a ta kasar Libya
2015-04-01 10:25:12 cri
A ranar Talatan nan, majalisar jama'ar kasar Libya da ke samu goyon baya daga wajen kungiyar masu kishin addini ta jefa kuri'u da tsaida kudurin sauke Omar al-Hasi daga mukaminsa na firaministan gwamnatin 'yantar da jama'a ta kasar Libya.

Kakakin majalisar jama'ar kasar Omar Hemeidan ya bayyana wa 'yan jarida cewa, 'yan majalisar 74 a cikin dukkan 'yan majalisar 85 sun amince da sauke Al-Hasi daga mukaminsa. Kana majalisar ta tsaida kuduri a wannan rana cewa, mataimakin firaministan gwamnatin ya gudanar da ayyukan firaministan kafin aka zabi sabo.

Amma Hemeidan bai yi bayani game da dalilin da ya sa aka sauke Al-Hasi daga mukaminsa ba. A kwanakin baya dai an zargi ministocin gwamnatin Al-Hasi da dama da cin hanci da rashawa, amma Al-Hasi bai sauke su daga mukamansu ba, don haka aka nuna rashin jin dadi game da hakan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China