in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron tattaunawa a tsakanin bangarori daban daban da rikicin kasar Libya ya shafa a birnin Algiers
2015-03-11 10:35:12 cri
A jiya Talata 10 ga wata a Algiers, babban birnin kasar Aljeriya, shugabanni da wakilan bangarori daban daban da rikicin kasar Libya ya shafa suka yi taro don tattauna yadda za a warware matsalar da kasar ke fama da shi a halin yanzu.

Wakilin musamman na babban satakaren MDD mai kula da batun Libya Bernardino Leon ya bayyana a gun bikin bude taron cewa, wannan taro yana da muhimmanci sosai, don haka tilas ne shugabannin bangarori daban daban na kasar Libya su yi kokarin shimfida zaman lafiya. Ana sa ran masu halartar taron za su bullo da matakan da za su kai ga warware rikicin kasar, da kafa tsarin demokuradiyya da kawar da ayyukan ta'addanci.

Ban da wannan kuma, Leon ya bayyana cewa, taron wata alama ce da ke nuna cewa, bangarori daban daban da rikicin kasar Libya ya shafa, sun fahimci cewa, yin shawarwari cikin lumana ita ce hanya mafi dacewa wajen warware rikicin kasar, ganin yadda ayyukan ta'addanci ke kara haddasa barazana ga samun dinkuwar kasar. Kana ya ce, MDD ta nuna goyon baya ga bangarorin kasar daban daban da su yi shawarwari ba tare da gindaya wani sharadi ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China