in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saurin karuwar tattalin arzikin Sin zai iya kai 7.2% a bana, a cewar bankin ADB
2015-03-24 20:17:49 cri
A yau Talata 24 ga wata, bankin bunkasuwar Asiya (ADB) ya fidda takardar hasashen bunkasuwar nahiyar Asiya a shekarar 2015, inda ya bayyana cewa, a sakamakon yadda gwamnatin kasar ta rage saurin bunkasuwar tattalin arzikin kasar, da kuma ci gaba da gudanar da shirin yin kwaskwarima, saurin karuwar tattalin arzikin Sin zai ci gaba da raguwa kadan a shekarar 2015 da 2016. Kuma bankin ya kiyasta cewa, yawan GDP na Sin zai karu da 7.2% a bana bisa na makamancin lokaci na bara.

A shekarar 2014, yawan karuwar GDP na Sin ya kai 7.4%. A cikin rahoton aiki da gwamnatin kasar Sin ta gabatar a wannan shekara kuma, an dasa wannan buri zuwa 7% a bana. Kafin wannan, firaminista Li Keqiang ya bayyana a gun taron manema labaru na manyan taruka biyu na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin da majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasa ta kasar cewa, kasar na da karfi wajen tabbatar da bunkasuwar tattalin arziki yadda ya kamata.

Game da yanayin da ake ciki a fannin tattalin arziki a yanzu kuma, rahoton bankin ADB ya bayyana cewa, a matsayinta na kasar da tattalin arzikinta ya fi karfi a Asiya, watakila Sin za ta ci gaba da kasancewa kasar da ta fi ba da taimako wajen samun karuwar GDP a duniya a shekarar 2015 da 2016. A sa'i daya, bankin ya yi kiyasin cewa, saurin karuwar GDP na Sin zai kai 7% a shekarar 2016 bisa na shekarar 2015.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China