GDP na kasar Sin ya karu da kashi 7.4% a farkon watanni ukun bana
Alkaluman da hukumar kula da kididdiga ta kasar Sin ta fitar a ranar 16 ga wata nan sun yi nuni da cewa, bisa kwarya-kwaryar kidayar da aka yi, ma'aunin tattalin arzikin kasar Sin na GDP, ya kai kudin Sin yuan biliyan dubu 12 da 820 a farkon watanni ukun wannan shekara da muke ciki, adadin da ya karu da kashi 7.4% bisa na makamancin wannan lokaci a bara, kuma karuwar da ta ragu da kashi 0.3% bisa na watanni ukun karshen shekarar 2013 da ta gabata. Mr.Sheng Laiyun, kakakin hukumar ta kididdiga ya ce, tattalin arzikin kasar Sin ya gudana yadda ya kamata a farkon watanni uku na wannan shekara, kuma kasar Sin tana da imani, da kuma kwarewa ta tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikinta cikin dogon lokaci.
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku