in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
GDP na kasar Sin ya karu da kashi 7.4% a farkon watanni ukun bana
2014-04-16 18:04:38 cri
Alkaluman da hukumar kula da kididdiga ta kasar Sin ta fitar a ranar 16 ga wata nan sun yi nuni da cewa, bisa kwarya-kwaryar kidayar da aka yi, ma'aunin tattalin arzikin kasar Sin na GDP, ya kai kudin Sin yuan biliyan dubu 12 da 820 a farkon watanni ukun wannan shekara da muke ciki, adadin da ya karu da kashi 7.4% bisa na makamancin wannan lokaci a bara, kuma karuwar da ta ragu da kashi 0.3% bisa na watanni ukun karshen shekarar 2013 da ta gabata. Mr.Sheng Laiyun, kakakin hukumar ta kididdiga ya ce, tattalin arzikin kasar Sin ya gudana yadda ya kamata a farkon watanni uku na wannan shekara, kuma kasar Sin tana da imani, da kuma kwarewa ta tabbatar da dorewar ci gaban tattalin arzikinta cikin dogon lokaci.
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China