in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Masar ya gana da manzon musamman na shugaban Sin
2015-03-15 15:01:07 cri
Jiya Asabar 14 ga wata, shugaban kasar Masar Abdelfattah al Sisi ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Sin, kana ministan harkokin kasuwancin kasa na Sin Gao Hucheng, wanda ya halarci babban taron raya tattalin arziki da aka yi a birnin Sharm el Sheikh na kasar Masar.

A yayin ganawarsu, Mr. Gao ya bayyana cewa, kasar Sin na mai da hankali da kuma goyon bayan kasar Masar wajen raya tattalin arzikin kasar, da kuma kyautata zaman rayuwar jama'a.

A nasa bangare, Abdelfattah al Sisi ya bayyana fatan alheri ga shugaba Xi Jinping, da nuna godiya sosai ga halartar ministan harkokin kasuwanci na Sin Gao Hucheng a wannan babban taron raya tattalin arzikin kasar Masar, tare da ba da jawabi a matsayin manzon musamman na shugaban kasar Sin.

Haka kuma, Abdelfattah al Sisi na maraba da halartar kamfanonin kasar Sin cikin ayyukan gina kasar Masar, kuma yana fatan karfafa hadin gwiwar kasashen biyu kan aikin gina kayayyakin more rayuwa da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China