in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 18 suka mutu a kasar Masar sakamakon tashe-tashen hankali
2015-01-26 15:16:47 cri
Ranar 25 ga watan Janairu rana ce ta cika shekaru 4 da aka hambarar da mulkin tsohon shugaban kasar Masar Mohammed Hosni Mubarak. A yayin bikin tunawa da wannan rana, an samu rikice-rikice a wurare daban daban na kasar Masar, wadanda suka haddasa mutuwar mutane a kalla 18.

Bisa labarin da jaridar Al-Ahram ta kasar Masar ta bayar a kan shafin Internet, an ce, wasu kungiyoyi masu goyon bayan tsohon shugaba Mubarak sun yi kira ga jama'a da su yi zanga-zanga a wannan rana. A yayin da kuma wasu mutane masu adawa da wadannan kungiyoyin suka yi fito na fito da 'yan sanda a wurare daban daban a kasar. Bisa labarin da ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Masar ta bayar, an ce, mutane a kalla 18 sun mutu a sakamakon rikice-rikicen. A ciki, yawan mutanen da suka mutu sakamakon rikicin da aka samu a birnin Alkahira ya kai 11, ciki har da wani dan sanda. Haka kuma an samu mutanen da suka mutu a sakamakon rikice-rikicen da suka barke a birnin Alexandria, da jahohin Giza da Beheira.

Kana ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Masar ta bayyana cewa, mutane a kalla 38 sun ji rauni a sakamakon wadannan rikice-rikicen. Tuni dai ma'aikatar harkokin cikin gida ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, an kama masu zanga-zanga kimanin 150. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China