Sa'an nan kuma shugaban kasar Masar Abdelfattah al Sisi ya sanar a ran 15 ga wata da dare cewa, kasarsa za ta dauki matakai yadda ya kamata dangane da lamarin kisan 'yan kasar da kungiyar IS ta yi garkuwa da su.
Kaza lika, fadar shugaban kasar ta Masar ta fidda wata sanarwa, inda ta nuna juyayi dangane da kashe wadannan mutane 'yan kasar guda 21 a kasar Libya, tare da ayyana zaman makoki na tsawon kwanaki 7 a duk fadin kasar.
A wannan rana, rashen kungiyar IS dake kasar Libya ya gabatar da wani bidiyo a shafin intanet dake nuna dakurun IS fuska boye suna kashe 'yan kasar Masar na darikar Copt guda 21. (Maryam)