in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ebola na haifar da kalubale ga tattalin arzikin yammacin Afirka
2015-03-13 10:41:53 cri
A jiya ne shirin raya kasashe na MDD wato UNDP ya fidda wani rahoto game da tasirin yaduwar cutar Ebola a yammacin Afirka ga tattalin arziki da zaman rayuwar yankin, inda ya nuna cewa, yaduwar cutar Ebola a yammacin Afirka ta haddasa matukar illa ga tattalin arzikin yankin, inda ya ce, za a yi asarar a kalla dala biliyan 3.6 a ko wace shekara daga shekarar 2014 zuwa 2017.

Bugu da kari, a cewar sabon rahoton da ofishin ya fitar, saboda huldar dake tsakaninsu da kasashe uku da suka fi fama da cutar wato Liberia, Saliyo dakuma Guinea, wasu kasashen da cutar ba ta kai gare su ba, su ma sun gamu da matsaloli da suka shafi raguwar cinikayya, rufe kan iyakokia, soke jadawalin zirga-zirgar jiragen sama, raguwar zuba jari da na sana'ar yawon shakatawa.

Don haka rahoton ya nuna cewa, ya kamata gwamnatocin yammacin kasashen Afirka da hukumomin yankin da abin ya shafa su ci gaba da taimakawa kasashen kan hana sake yaduwar cutar a yankin, kana da sake gina kasa, da kuma daukar matakan da suka hada da inganta ayyukan cibiyoyin lafiya, kafa cibiyoyin yin rigakafi da hana yaduwar cututtuka, kula da harkokin iyakokin dake tsakanin kasashen da kuma kafa tsarin yin rigakafi da daukar matakan gaggawa da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China