in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta fara duba lafiyar fasinjojin da za su bar kasar ta jiragen sama
2015-03-09 14:47:01 cri
Ministan lafiya na Najeriya Onyebuchi Chukwu ya bayyana shirin kasar na fara duba lafiyar fasinjoji kafin su tashi daga kasar ta jiragen sama, a matsayin wani mataki na hana yaduwar cutar nan ta Ebola da yanzu haka ke yaduwa a sassa daban-daban na duniya.

Ministan wanda ya bayyana hakan ranar Alhamis yayin wani taron manema labarai a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya, ya ce, za a fara aiwatar da shirin duba lafiyar fasinjojin ne a mako mai zuwa yayin da aka himmatu wajen samar da dukkan abubuwan da ake bukata, kamar ma'aikata da kayayyakin aiki.

Chukwu ya kuma shaidawa 'yan jaridun cewa, darasin da Najeriya ta koya ya kara bude wa kasashen duniya ido game da tabbacin cutar ta Ebola, wadda ya zuwa wannan lokaci ta halaka mutane biyu a Najeriya.

Najeriya ta yanke shawarar fara duba lafiyar fasinjoji kafin su bar kasar ne kasa da sa'o'i 24 bayan da kasar ta Najeriya ta ayyana dokar ta baci game da cutar Ebola, ganin yadda yanzu kowa a duniya ke cikin barazana.

A cewar hukumar lafiya ta duniya WHO, mutane 1,711 ne suka kamu da cutar, kana 932 suka mutu a wannan shekara a cikin kasashen Guinea, Liberia, Najeriya da Saliyo. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China