in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Maras lafiya na karshe da aka tabbatar ya kamu da Ebola ya fito daga cibiyar jinya a Liberiya
2015-03-06 15:20:47 cri

Kasar Liberiya ta sallami maras lafiya na karshe da ya kamu da cutar Ebola daga wata cibiyar kasar Sin dake kula da masu fama da cutar Ebola (ETU).

A halin yanzu babu mutum guda har zuwa wannan rana da aka tabbatar ya kamu da Ebola a cikin cibiyoyin jinya 19 na ETU dake Liberiya. A yayin wani gajeren bikin da aka shirya a Monrovia, shugaban ETU na kasar Sin, kanal Yang Haiwei, ya bayyana cewa, maras lafiya guda da aka tura asibiti a ranar 18 ga watan Febrairun shekarar 2014 yana cikin hali mai tsanani a lokacin. Amma bayan kwanaki 15 da samun jinya daga tawagar likitancin kasar Sin, a karshe wannan maras lafiya ya samu sauki, in ji mista Yang, tare da bayyana cewa, yana daga cikin mutanen da aka ceto rayukansu a cibiyar ETU ta kasar Sin. Amma kuma duk da haka ya yi kashedi kan illolin da za su biyo baya idan har ba'a girmama matakan da suka shafi Ebola ba a wuraren da ake fama da cutar a kasar.

Wannan nasara da aka samu za ta iyar kasancewa ta 'dan lokaci, amma duk da haka wani muhimmin mataki ne. Tawagar likitancin kasar Sin za ta ci gaba da ba da nata kokari domin yaki da cutar Ebola, in ji mista Yang. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China