in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan bangarori biyu masu rikici da juna a Sudan ta Kudu su cimma matsaya tun da wuri
2015-03-10 20:27:08 cri
A yau Talata 10 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje na Sin, Hong Lei ya bayyana ra'ayin kasar game da batun rashin cimma matsaya daya kan daddale yarjejeniyar shimfida zaman lafiya tsakanin bangarori biyu da suke rikici tsakaninsu a kasar Sudan ta Kudu, inda yace Sin na fatan bangarorin biyu za su yi la'akari da babbar moriyar kasa da ta jama'a, su yanke shawara yadda ya kamata, domin cimma matsaya tsakaninsu cikin lokaci.

A ranar 6 ga wata, shugabannin bangarorin biyu na Sudan ta Kudu ba su kai ga rattaba hannu kan yarjejeniyar tabbatar da zaman lafiya ta karshe ba, a don haka, yunkurin shimfida zaman lafiya a kasar ya sake samun tsaiko. Shugaban kungiyar gwamnatocin gabashin Afrika"IGAD", kuma firaministan kasar Habasha, Hailemariam Dessalegn ya ba da sanarwar, inda ya bayyana bakin cikinsa kan sakamakon da aka samu.

A game da wannan batu, Hong Lei ya ce, kamata ya yi kasa da kasa su ci gaba da nuna goyon baya ga kokarin kungiyar "IGAD" na shiga tsakani. Kuma kasar Sin na fatan ci gaba da yin mu'amala da kungiyar da kuma sauran hukumomin dake kokarin shiga tsakani kan wannan batu, a kokarin sa kaimi ga daidaita batun Sudan ta Kudu tun da wuri.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China